|
|
Makarantar
Alkura'ani
|
Makarantun Alkur'ani a kasar Hausa sun kasu kashi
biyu. Kashi na farko shine inda ake koyawa yara karatun Alkur'ani
kawai ba tare da hadda ba. Kashi na biyu kuwa shine inda ake
karantarwa hade da hadda. Bari mu fara da kashi na farko domin
shine matakin farko, kuma shine ya fi yawa a duk fadin kasar
Hausa. Ana sa yaro ko yarinyu Makarantar Alkur'ani ne lokacin
da suka cika shekara biyar. Ana kiran irin wannan Makaranta
da sunan Makarantar Allo, domin a cikinta ne yara ke koyon karatun
Alkur'ani kuma a kan Alluna ake koya masu rubutu da ka m t u.
Wadannan makarantu basu da iyaka domin da wuya a sami magidanUi
rnnsu 'ya'ya da zasu barsu hakabatareda ansakasu a Makarantar
Allo ba.
Malamin da yacancantayabude Makarantar Allo shine wanda zai
iya karanta Alkurani dukkansa kuma ingataccen karatu, ya kuma
haddace a kalla izifi daya, misali daga surar Sabbi zuwa Nasi.
Yadda ake karantarwar kuwa shine Malami zai fara rubutawa yara
haruffan Alif, Ba. Ja, Da, ba tare da wasali ba. Idan yaro ya
sansu sai a rubuta masa surar Fatiha, ita ma bada ' wasali ba,
sannan a koya masa fadar haruffanta har ya sansu. Daga nan sai
aci gaba zuwa surar Nasi, sai Falaki, sannan Kulhuwa, sai Tabat
yada, sai Iza ja'a, haka dai har sai dalibi ya kai surar Wailul
Likulli. Daga nan sai a sake dawo da dalibi kasa a rubuta masa
Fatiha da Wasulla ana koya masa yadda ake tada baki har sai
ya san duk surorin nan ya kuma haddace su. Daga nan sai ayi
ta rubutawa dalibi surori ana koya masa tare da hadda har sai
ya kai Sabbih. galibi daga nan ne dalibi zai daina hadda sai
ya yi ta karanta surori bayan an rubuta masa aAllo har sai ya
kai Amma. Hakanan dai tafiya sai ta mika ya yi tayi har ya sauke
Alkur'ani. A tsakanin wannan lokaci ne dalibi zai koyi rubutu
da kansa bayan ya gama sai Malaminsa yayi masa abinda ake kira
Safi, ya huta ke nan dawahalar rubutu.
Wannan hanya takan dauki dalibi kimanin shekaru hudu ko fiye
da haka kafin ya sauke Alkur'ani. Akwai wasu surori ko hizifai
da iadan dalibi ya kai garesu Malami yakan nemi mahaifin yaron
da yayi masa sadaka ta abinci ko ya yanka Akuya ko Rago. Bisa
ga al'ada wannan sadaka gidan Malami ake kaiwa. Dalilan da aka
bayar na kaiwa Malami sadaka shine domin ba kasafai iyayen vara
ke baiwa Malaman Allo Iadan karantarwar da suke yiwa 'ya'yansu
ba. Malam kan ce wai idan ba'a yi wannan sadakr ba dalibi na
zama wawa ko dakiki. Idan yaro ya sauke Alkur'ani sai kuma mahaifinsa
ya shirya babban taro ko liyafa inda ake gayyatar 'yanuwa da
abokan arziki su zo su albarkaci wannan yaro. Ana cikawa Malamin
yaron aljihunsa da kudi. |
|
{talla} |
|
|
|