Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

Aiki A Karkara 


  Kamar yadda aka sami wahala kafin ilmin Boko ya sami karbuwa a biranen jihohin Arewa, haka abin ya kasance a kauyuka. lyaye suka rika boye 'ya'yansu basa son su kaisu Makarnta, sun gwammace su bar 'ya'yansu suyi masu aikin gona. Wasu kuma a tura su Makarntun Allo daga nan ne wasu ke sullebewa su gudu zuwa birane. Kamar yadda aka yi bayanin tsarin Makarantun Allo a baya za'a fahimci cewa ba'a yi maganar ci rani da dalibai ke barin kayuka zuwa birane ba. Shi dai ci rani baya kara komai sai lalacewar dalibai. Mafi yawa daga cikin daliban da suke zuwa birane ci rani basa yin karatun sai dai neman abinda zasu ci da wanda zasu kaiwa malam gida. Yawon ci rani dai ya sami asali ne daga matasa wadanda bayan sun kammala aikin gona suke kokarin shiga birane don kadar raba, idan damuna ta fadi su koma kauyu-kansu. A shekarun baya, aPamarin yana da dan kyau ba kamar yanzu ba. A baya can ana samun albarkar gona mai yawa, kuma kayan abinci bashi da tsada. Da kudin da manomi ya saida amfanin gonarsa ne yake yiwa 'ya'yansa da matansa sutura da sayen kayan abinci. Shi yasa basa son barin 'ya'yansu zuwa Makaranta don kada a rage masu ma'aikata a gonakinsu. Halin rayuwa a karkara a yanzu ta lalace saboda tabarbarewar tattalin arziki da harkokin noma. Babu isassun kayan abinci kamar da. Babu wuraren shakatawa a karkara kamar yadda ake dasu a birane.

Bayan da hukumomi suka sami nasarar wayar da kan jama'a a kauyuka wajen tura 'ya'yansu makarantu sai wasu matsalolin suka taso. Wadannan matsaloli kuwa sun hada da gina makarantu, samar da kayan aiki, Malaman da zasu koyar da kuma ayyukan yi bayan yaran sun kammala makaranta. Idan ya rage watanni uku daliban Makarantun horad da Malamai su kammala karatunsu na TITISI, babu abinda yake ran Malami sai tunanin inda za'a kaishi yayi aikin koyarwa. Amma saboda rashin kayan jin dadin rayuwa a kauyuka mafi yawa daga cikin Malaman makarantun Boko basa son zuwa kauye don su koyar. Shi yasa halin da makarantun boko a kauyuka suke ciki bashi da kyaun gani. Babu isassun kayan aiki a makarantun kauyuka, babu abin zama, babu gidajen kwanan Malamai da dai sauransu. Gashi kuma idan aka yi la'akari da yawan haihuwa da ake yi a kauyuka za'a ga cewa ana bukatar yin gyara sosai-da sosai a makarntun boko dake karkara don a kwadaitawa Malamai zuwa kauye su koyar. Malaman boko da suka amince da zuwa kauye su koyar suna haduwa da matsalar abinci, shi yasa ake ganin zai yi kyau Malamin Makarantar boko a kauye yayi kokarin koyon yadda ake dafa abinci idan bashi da mata wadda zata dafa masa. Giggina Makarantun da aka fara yi a kauyuka, ya kamata aci gaba da yi, sannan a gyara wadanda ake dasu don samar da gurbin wasu daliban. Majalisun kananan hukumomi su inganta hanyar da suke bi wajen samar da kayan aiki a makarantun karkara ta yadda dalibai da su kansu Malamai zasu ji dadin yin nazari. Sai kuma maganar samun Malaman da zasu koyar. Kamar yadda aka bayyana a baya cewa daliban kolejojin horon Malamai basa son zuwa kauye ya kamata a gyara wannan matsayi domin rashin zuwa kauyen da Malamai keyi ya faru ne saboda rashin hanyoyin jin dadin rayuwa kamar ta birni. Su kansu daliban da suka fito daga kauyuka basa son komawa can suyi aikin koyarwa saboda wadannan matsaloli da aka bayyana.

Shawarar da za'a ba Malamin makarantar boko ita ce ya hakura ya tafl kauye ya koyar duk da cewa akwai matsaloli. Gefe guda kuma hukumomin da abin ya shafa su dukufa wajen neman hanyoyin kyautata rayuwar karkara. Tunda matsaloli ne ke hana Malamai zuwa kauyuka ya kamata a kokarta kauda wadannan matsalolin. A samar da gidajen kwanan Malamai, kekunan hawa da kyautata albashin Malamai tare da biyansu a kan lokaci. Malamin makaranta idan yayi hakuri ya tafi kauye yana koyarwa bayan ya shekara biyu zuwa uku sai a sauya masa wuri zuwa birni, idan kuma yaji dadin zama a kauyen sai a kyale shi a can. Muddin Malamin makaranta yace ba zai fita kauye ya koyar ba waye ke nan zai koyawa 'ya'yanmu dake kauyuka ilmi? Mafi yawa daga cikin kasashen da suka ci gaba a duniya Malaman Makarantunsu duk a karkara suke aikin koyarwa, kuma ana kyautata masu sosai yadda ya kamata.
 
{talla}

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka [email protected]

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.