Hausa Hausa English
Wakokin Hausa

Chat Room
Check your mai

Classified Ad

Jaridu


Mahada

 

 

 

 

kimiyyar Sararin Samaniya 


 
 
  Dawainiyar “Bincike”, sirke da “Kimiyya” ta kan jirkita ta kuma juya halin ilmin halittu da na tasawirorinsu. ‘Dauki misalin nazarin Sararin Samaniya ba tare da Kimiyya ba; sannan ka gwada shi da nazarin da aka yi shi tare da Kimiyya da irin sabbin damar da ta kawo na sauk’ak’ar da Bincike da fahimtar ma’anarsa.

‘Daya daga cikin baiwoyin da Allah (swt) Ya ba wa wasu mutane, ita ce baiwar “Bincike” da son bin k’wak’waf, wad'anda himmarsu da kwad’ayin neman saninsu suke yi masu jagora a kan wannan d’arika ta neman ilmi. Sakamakon wannan fafutuka tasu ita ce ilahirin riba da ci-gaban 'Dan-Adam, tun daga farkon lokaci. A cikin wannan d’awainiya, mutum ya kan shirya halayen tafiye-tafiye da burin k’osarda bukatunsa; ko don kan sa, ko jama’arsa, ko don al’ummar 'Dan-Adam gaba-d’ayanta. Yawon duniya, harin yak’i don ganima, tijara, farauta, hijira, hajji, duk d’awainiya ne da 'Dan-Adam yake yi don biyan bukatunsa, ko kuma cika umarnin addini ko na jama’a. A kowane hali na tafiye-tafiye, sabon ilmi yakan wanzarda kan sa a cikinta, in dai an yi nazari mai zurfi tare da auna manufar tafiyar ita kan ta.

A cikin tarihi, mun karanta labaran mashahuran mutane wad'anda suka yi d'awainiya a rayuwarsu don binciken sabon ilmi; kuma yawanci sukan tunkari matsaloli masu wahala a cikin wad'annan tafiye-tafiye nasu. Labaran mutane irinsu Alekzandara-za-gret (wanda wasu ke kuskurarren zaton shine Zurqallaini), Kolumbas, Vasco da Gama, Agha-Khan da sauransu, duk labarai ne na mabud’an ilmi da gwagwarmaya iri-iri. Rayuwar Manzon Allah, Muhammad (saw), da ta yawancin annabawa da waliyan addinai, kyawawan misalai ne na gwagwarmayar 'Dan-Adam da sadaukarwa don ilmantarwa. Haka muka ga bazuwar addinin musulunci ta zama mabud’in ilmi iri-iri a ko’ina a duniya, bayan kafa addinin shi kan sa. Idan muka karanta ayoyin Kimiyya a cikin Al-Qur'ani mai-tsarki, muka kuma yi nazari a kansu, ba shakka za a fahimci abin da nake nufi anan. Ashe dai tarihin 'Dan-Adam gaba d’ayansa, tafiyace cikin wannan himma ta neman ilmi; tun ana yin ta a k’as, ta koma kan dabbobin hawa, sannan a jirgin ruwa, har ga shi an kai shiga ko aika kumbuna masu ziyara da shawagi a Sararin Samaniya. Duk wad'annan ci-gaba na ababan sufuri, sakamakon bincike ne da Kimiyya, bayan alhairi na ilmin da aka tarar a dukkanin guraren da aka je.

'Dan-Adam ya fara d'awainiyar bincikensa ne tun ya na d’an-jariri a doron wannan ‘yar duniya tamu wadda Al-Qur'ani yake kira, Ard’, wadda kuma da can mutum ya zaci ba ko’ina a Sararin Samaniyar sai ita. Tun ya na zaton cewar “daben turb’aya” ce a shifid’e a mik’e tamkar darduma, har dai ya fahimci cewar a kewaye take kuma a dunk'ule take tana lilo ita kad’ai tamkar tamaular da aka lula sama. Da ya fahimci wannan, sai 'Dan-Adam, ya shiga d'awainiyar binciken ilmin k’asashe, tekuna da koguna, da duwatsun dake kan doronta, muhallinsu da kuma dalilan da suka sa ba sa fad’owa. A cikin wannan tafiya ta bincike, sai ya fara lura da irin mutane, dabbobi da tsirannin dake cikinta, kuma wannan fafutukar har yanzu ba ta k’are a gunsa ba. 'Dan-Adam ya na dad’a tsufa, bukatun rayuwarsa da kuma tilastuwar bincike don k’osardasu, suna k'ara yawa. Idan muka tuna, tun kafin balagarsa ne, mutum ya fahimci muhimmancin neman sabbin muhallai wad'anda zai iya bak’unta koma ya mallake ya kuma mamaye.

Don hakane ma ya shiga binciken budurwoyin k'asashe inda zai koma ya kafa rayuwarsa da kuma ta zuri’o’insa. Wannan ta baza 'Dan-Adam kusan ko’ina a kan doron duniyarsa, ta kuma haifarda sabon ilmi da muhimmancin albarkar k'asa, wadda ita kuma ta zama sabon dalilin wasu tafiye-tafiyen, yak’e-yak’e, hijira da tijara. Cikin lokaci, sai bak’i a wasu gurare, suka kai sabbin abinci, al’adu, ilmi, siyaysa -har ma da addinai- ga k'asashe da al’umun da suka bak’unta. Har-wa-yau kuma, a wasu guraren, bak’in suka maishesu mazauninsu ko guraren huld’arsu, koma a yawancin lokatai, na mallakarsu.

Zamanin da mutum yake kan gayar bincikensa, wannan duniya, ba shakka, ta ga canje-canje irin yadda ba za a sake gani ba. Daga dalilan k’osarda k’ishirwar ilmi, har aka kai na k’osarda bukatun rayuwa da danniya, har sai da bak’o yazo yafi d’an-gari bajinta a garinsu. Turawa, Larabawa -sannan mutanen Sin- duk sun yi rawar ganinsu a wannan harka ta baza bazarsu duk inda fuka-fukansu zasu iya zuwa. Ba shakka, har izuwa yau, k’urar da suka tayar a gurare masu nisa ba ta k’are bajewa ba. Duk wannan a sunan binciken sabbin tasawirori, gab’ob’i da iyaku; neman ilmi, dukiya da sabbin muhallai. Amma duk da haka, tasirin wannan d'awainiya ta bincike ba ta raunana ba, illa ma k’arfafa da tayi cikin imanin cewar ba ta da bambanci da makomar

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

{talla}

Littatafan Hausa

 
Gidajen Rediyo Hausa

 

 

       
 

Mohammed Hashim Gumel ya tsara ya gina wannan shafi. Kofar mu a bude take bisa duk wasu shawarwari da kuma ra'ayoyinku, kan wannan fili, da kuma irin abinda kuke so mu rika wallafawa."Gyara kayanka bai zama sauke muraba ba." Ana iya aiko mana da wasika ta layi kamar haka [email protected]

@Gumel.com 1998 Wannan fili an kareshi da dokar wallafawa, a nemi izzini kafin amfani da kayan mu.